APC tazo karshe a jihar Edo ~Atiku
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yaba da nadin Gwamna Nyesom Wike na Ribas a matsayin shugaban kwamitin yakin neman zaben Gwamnonin jihar Edo na jam’iyyar PDP. Mista Abubakar ya kuma yaba da nadin gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Fintiri a matsayin mataimaki ga Mista Wike a kan kwamitin Yakin. Da yake mayar da dayake magana game da nadin a cikin wata sanarwa a ofishinsa na harkokin watsa labarai na Abuja, Tsohon Mataimakin Shugaban ya ce: Gwamna Wike fitaccen mutum ne kuma dan kishin jam’iyya wanda yayi aiki domin nasararmu a jam’iyyar. ” A cewar Mista Abubakar, “Wike ya cancanci wannan muhimmin aiki, musamman a wannan mawuyacin lokacin da kasar ke matukar bukatar canji daga halin kuncin rayuwa da ake ciki a yanzu.”
Tsohon Mataimakin Shugaban yayi bayanin cewa “saboda rawar da ya taka shi Wike, ba ko shakka a zuciyata cewa yana da abinda zai iya jagorantar sake farfadowa, da sake fasalin PDP domin nasara a jihar Edo.” Ya yi kira ga dukkan shugabannin PDP da mambobin kungiyar da su ajiye bambance-bambance na mutum su kuma yi aiki tare da shi domin samun nasarar aiwatar da wannan muhimmin aiki. A cewar Atiku, “ya kamata mu hada karfi da karfe a wannan aiki ta hanyar sauke nauyin da ya rataya a wuyan gwamna Wike a kokarin dawo da jihar Edo da mayar dashi kan tafarkin ci gaba mai girma.” Tsohon VP ya lura cewa PDP ita ce jam’iyya daya tilo da ke da babban roko na kasa kuma yana da karfin ceto hadin kan mu da dawo da imani a cikin kungiyarmu ta kasa baki daya..