Labarai

Ga kadan daga Tarihin budurwa Halima Atete

Spread the love

Halima Yusuf Atete wacce aka fi sani da Halima Atete (an haife ta a 26 ga watan Nuwamba 1988) ‘yar fim ce a masana’antar Kannywood hausa
kuma furodusa ce, haifaffiyar garin Maiduguri ce da ke jihar Borno.
Halima Atete sananniya ce a masana’antar fim ta kannywood a kan rawar da take takawa a koyaushe a matsayin mai ɓarna da kishi. [2] Ta shiga masana’antar kannywood ne a shekarar 2012,

ta fara fitowa a fim din Asalina (Asali na) wanda ta shirya, bayan fitowar ta a fina-finai da dama kamar irin su Kona Gari, Asalina, Dakin Amarya, ta lashe kyautar sabuwar jaruma mafi kyau na City People Entertainment Awards a 2013, Na
kungiyar labarai ta London Voice of Africa kan kyakkyawan kwazonta a masana’antar ta nishadi.

An haifi Halima Atete a garin Maiduguri, jihar Borno. Ta yi makarantar firamare ta Maigari, ta kammala makarantar sakandaren gwamnati ta Yerwa. Halima ta sami diflomar kasa a fannin shari’a da kuma shari’ar farar hula. Halima Atete ta shiga masana’antar fim ta kannywood a shekarar 2012,
ta fito a fina-finai sama da 160, sannan kuma ta samar da fina-finai da dama.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button