Gwamna Abba na Kano ya rattaba hannu kan kasafin ku’din gaggawa na naira bilyan N58.1bn domin cigaba da Ayyuka ga Al’ummar jihar Kano.

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu a kan karin kasafin kudin shekarar 2023, wanda ya kai N58,191, 535, 018.12.
A yayin da yake gabatar da kasafin kudin, Gwamna Yusuf ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa za ta bi ka’idojin da suka shafi kasafin kudi.
A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya fitar, Yusuf ya tabbatar da cewa za a yi amfani da kudaden da aka ware bisa ka’ida ta gaskiya da gaskiya.
Wannan karin kasafin kudin an yi shi ne domin a kula da ci gaban ababen more rayuwa da kasafin kudin shekarar 2023 bai kama su ba domin biyan bukatun al’ummar jihar Kano,” Gwamnan ya bayyana.
“Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yaba da kokarin Kwamishinan, Tsare-tsare da Kasafin Kudi na gaggauta aiwatar da takardun kasafin kudin ga majalisar dokokin jihar,” in ji sanarwar.
Tun da farko, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibrin Ismail Falgore wanda ya jagoranci manyan jami’an majalisar da kwamitinta na kasafin kudin, ya gabatar da kudirin amincewa a gidan gwamnatin Kano na Africa House.
Gwamnan ya kuma bukaci a ci gaba da ba da goyon baya da kuma kyakkyawar alaka a tsakanin bangaren zartarwa da na majalisar dokoki a jihar.