Labarai

Gwamna El rufa’i ya bayarda umarnin Bude makarantun jihar kaduna

Spread the love

Gwamnatin Jihar Kaduna ta sanar da ranakun komawa makarantu, kwanaki kadan bayan da wasu jihohin suka koma Makarantu gadan-gadan.

A daren yau Laraba ne Gwamnatin ta fitar da sanarwar, wanda Al’umma suka dauki haka a matsayin bazata.

Gwamnatin ta bayyana ranakun 18 da 19 na wannan watan na Okyoba a matsayin wanakin komawa makarantun.

Sai dai ba gabaki daya makarantun zaa koma ba, yan aji 6 na makarantar Firamari da yan aji biyar SS2 na makarantun sakandare da yan aji biyu JSS2 na makarantun karamar sakandare ne zasu koma a makon gobe.

Makwanni biyu baya, Yan JSS 1 da yan SS1, suma zasu bi sahun dalubai wajen koma makarantun.

Rahotan bai bayyana ranakun da daluban Nazare da Firamari zasu koma makarantu ba. DIMOKURADIYYA:

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button