Gwamna Masari Yace yayi magana da ‘yan ta’addan da Suka sace daliban kankara.
Gwamnan jihar Katsina, Aminu Masari, ya ce wadanda suka sace akalla dalibai 333 na Makarantar Sakandaren Kimiyya ta Gwamnati, dake Kankara, sun tuntubi gwamnatinsa.
Ya bayyana hakan ne lokacin da yake yi wa shugaban kasa bayani, Manjo Janar Muhammadu Buhari (mai ritaya), a Daura ranar Litinin.
Wannan ya na kunshe ne a cikin wata sanarwa daga babban hadimin shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai Garba Shehu.
Sanarwar ta karanto, “Shugaban kasa Muhammadu Buhari ranar Litinin a garin Daura, jihar Katsina, ya karbi karin bayani kan yaran da aka sace daga Makarantar Sakandaren Kimiyya ta Gwamnati, Kankara, tare da tabbaci daga Gwamna Aminu Bello Masari na ci gaba mai dorewa don fitar da su ba tare da cutarwa ba.
“Gwamnan, wanda ya samu rakiyar Mataimakin Gwamnan Jihar, Manir Yakubu, ya ce masu satar mutanen sun tuntuba kuma tuni an tattauna game da tsaro da komawa gidajensu.
Gwamna Masari ya kuma lura cewa hukumomin tsaro sun gano matsayin yaran.
Gwamnan ya ce Shugaban kasar ya dukufa wajen ganin an ceto yaran makarantar, ya kara da cewa ya dace kawai a ziyarci Shugaban kasar a ba shi cikakken bayani game da kokarin kubutar da su. ”
‘Yan fashin sun mamaye makarantar ne a daren Juma’a inda suka yi awon gaba da daliban bayan sun yi artabu da‘ yan sanda. Shugaban ya isa jihar ne a ranar Juma’a, sa’o’i kafin sace su