Kasashen Ketare

Gwamnatin Amurika ta bukaci Gwamnatin Buhari da Takawo karshen Zubda Jini a Arewacin Kasar Nan.

Spread the love

Ahmed T. Adam Bagas

Ma’aikatar Harkokin wajen Amurika tayi kira ga Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari da ya kawo karshen Kashe kashen da Yazama tamkar Ruwan dare ne a Arewa cin Kasar.

A sanarwar da ma’aikatar ta fitar tace Kungiyar dake Kokarin kafa daular Islama a Yammacin Afrika ISWAP Ta kashe Sama da mutane 120 a Borno.

Har Ila yau tace ko a Ranar 1- ga Satan Yuni yan Ta’addan sun kashe Limami da mai gari a Borno, sannan Ranar 9-ga watan Yuni an kashe wani Pasto da matarsa mai Juna Biyu a Taraba.

Sannan ga kisan da A kayi Na kwannan a Garin Kadisau ta Jahar Katsina Wanda yayi sanadiyar Kashe Sama da mutum Hamsin a Garin, Wanda hakan yayi sanadiyar Matasan Yankin Shiga zanga Zangar Lumana Na kin amincewa da Kisan da yan ta’adda keyi a Yankin Arewa.

A Shekaran Jiya mah Kungiyar dake Rajin Kare hakkin Dan Adam AMNESTY INTERNATIONAL Ta Ce Gwamnati Buhari Ta kasa Kare Rayukan Al’ummar ta.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button