Gwamnatin Amurka tayi Allah Wadai da Gwamnatin Nageriya da Jami’an tsaron Soja bisa kisan masu Zanga Zangar #Endsars
Gwamnatin Amurka ta yi Allah wadai da harbe-harbe da kisan masu zanga-zangar nuna kin jinin ‘yan sanda a Legas. A ranar Talata ne Sojojin Najeriya suka bude wuta kan masu zanga-zangar lumana, inda suka kashe a kalla mutane 12 a cewar Amnesty International. A cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, Amurka ta ce ta yi Allah wadai da amfani da karfi fiye da kima da sojoji suka yi wa masu zanga-zangar da ba su dauke da makami a Lagos, wanda ya yi sanadiyyar mutuwa da raunata wasu da dama
“Muna maraba da binciken gaggawa game da duk wani amfani da karfi fiye da kima da mambobin jami’an tsaro suka yi. “Wadanda suke da hannu ya kamata a yi masu hisabi kamar yadda dokar Najeriya ta tanada. “’Yancin taron cikin lumana da’ yancin faɗar albarkacin baki sune mahimman ‘yancin ɗan adam da kuma manyan ƙa’idodin dimokiradiyya. “Muna kira ga jami’an tsaro da su nuna matukar kamewa da mutunta hakkoki na asali ga masu zanga-zangar su kasance cikin lumana. Muna mika ta’aziyyarmu ga wadanda rikicin ya rutsa da su da iyalansu. ”