Tsaro

Ka Yarda Mu Shigo Najeriya Zamu Karar Da ‘Yan Boko Haram A Cikin Sati Biyu___Shugaban Kasar Chadi Idris Deby Ya Fadawa Shugaba Buhari.

Spread the love

Shugaban kasar chadi idris deby ya yi kira ga shugaban kasar Najeriya Muhmammadu Buhari da ya bashi dama ya shigo Najeriya zai yaki boko haram a duk inda suke lungu da sako na cikin kasar, kuma zai gama dasu acikin sati biyu kacal.

Idris Deby ya yi wannan furucin ne yayin da yake mika sakon jaje ga gwamnan borno Babagana Umar Zulum, da sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a harin kwanton bauna da ‘yan Boko Haram suka kaiwa ayarin motocin gwamna Zulum.

Idris deby yace mafakar boko haram ba wata boyayyiya bace, kuma masu daukar nauyinsu ma a bayyane suke, don haka muna kira a gareka da ka bamu ragamar yakin mu shigo cikin kasar, za ka ga aiki da cikawa, inji shi.

Masu karatu me zakuce game da wannan tayi na Shugaba Idris Deby ga Shugaba Buhari?

Daga Kabiru Ado Muhd

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button