Lafiya

Kasashen Duniya Na Fargabar Dawowar Corona Virus karo Na biyu…

Spread the love

Daga Ahmed T. Adam Bagas

Sakamakon fargabar sake bullar cutar tasa an kulle kasuwannin Dillalan Kayan Abinci shida a Beijing babban birnin China, Kuma an sake dage Lokacin komawa makarantu.

A wannan makon ne dai aka Sassauta Dokar kulle a kasar India sai dai a kulli yaumin akan samu Karin mutane masu dauke da Cutar a Kasar.

A Korea kuwa an dauki matakan kariya da kamuwa da Cutar da Muhalli domin Gudun yawaitar Cutar.

A Rasha kuwa Akwai fargabar Sake Barkewar Anobar kasancewa Kasar Itace ta Uku wajen masu Yawan Cutar a Duniya.

A Nageria ma dai Duk da Sassauta dokar da Akayi a kulli yaumin Ana samun Karuwar masu dauke da Cutar kamar yadda Hukumar dake kula da Cututtka masu yaduwa ta Kasar NCDC take Sanarwa kullum.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button