Kasashen Ketare

A Yau Laraba Akayi Jana’izar Sarkin Kuwait Al-Ahmad Al-jaber Al-sabah.

Spread the love

Sarkin Kuwait Al-Ahmad yana daya daga cikin sarakunan kasashen daular larabawa da yayi fice wajen tsayawa tsayin daka don ganin kasashen turawan yamma musamman kasar Isra’ila sun daina takurawa kasashen musulmi da hare haren ta’addanci.

Yana daya daga cikin sarakunan daular larabawa da yayi ikirarin yanke Hulda da kasar Isra’ila matukar bata daina takurawa kasashen musulmi da hare haren ta’addanci na babu gaira babu dalili ba.

Sarkin Kuwait ya yi fice wajen karbar ‘yan gudun hijira daga ko wacce kasa ta musulmi da hare haren ta addanci yaci su, ya dawo dasu cikin kasarsa ta kuwait yaci gaba da basu kulawa.

Duniyar Musulunci ta yi matukar yaba masa wajen shige da fice da ya ringa yi a tsakanin kasashen da harin ta’addanci ya addaba don ganin musulman yankunan sun sami ‘yanci na zaman lafiya kamar kowa.

Muna rokon Allah Ubangiji yajikansa da Rahma yasa mutuwa ta zamo Hutu agareshi Ameeen ya Rabbi.

Daga Kabiru Ado Muhd.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button