Rahotanni

Ku cigaba da zama a Ondo, domin jihar ku ce, gwamnan Ekiti Kayode ya fadawa Fulani.

Shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya kuma Gwamnan jihar Ekiti Kayode Fayemi, ya bai wa Fulanin da ke zaune a jihar Ondo tabbacin cewa babu abin da zai sake samun su.

Inda ya ce su kwantar da hankalinsu, jihar Ondo gidansu ne, suna da ‘yancin Zama cikin Salama a Jihar.

Har wa yau ya yi gargadin a daina kabilantar da matsalar tsaron kasarnan, domin a cewarsa, matsalar ta shafi kowacce kabila a Nijeriya Inji Fayemi.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button