• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
JaridarMikiya
Advertisement
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
    • Home – Layout 6
  • Tech

    These Are the 5 Big Tech Stories to Watch in 2017

    With 150 million daily active users, Instagram Stories is launching ads

    Trending Tags

    • Nintendo Switch
    • CES 2017
    • Playstation 4 Pro
    • Mark Zuckerberg
No Result
View All Result
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
    • Home – Layout 6
  • Tech

    These Are the 5 Big Tech Stories to Watch in 2017

    With 150 million daily active users, Instagram Stories is launching ads

    Trending Tags

    • Nintendo Switch
    • CES 2017
    • Playstation 4 Pro
    • Mark Zuckerberg
No Result
View All Result
JaridarMikiya
No Result
View All Result
Home Kunne Ya Girmi Kaka

Hujjojin Dake Nuna Asalin Hausawa Daga Misira Suke.

Sabiu1 by Sabiu1
June 7, 2020
in Kunne Ya Girmi Kaka
0
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Littafin ‘Gamsasshen Asalin Hausawa Da Harshensu’ Wanda Comrade Zakariyya Abdurrahman Shu’aibu Kabo Ya Wallafa A Shekarar 2013.

Daga Sadiq Tukur Gwarzo.

Kashi Na ɗaya.

SALSALAR BAHAUSHE
Marubucin wannan littafi ya tafi akan cewa:- Jinsin Zangiy ɗan Nuhu sune mazauna Afirka ta yamma da tsakiyar ta da kuma Kudancinta.

Sai dai dangane da masu danganta cewa jinsin bakin mutum ya fito ne daga Hamu ɗan Annabi Nuhu A.S wannan kuskure ne, har suke cewa wai an samu saɓani ne sai Annabi Nuhu yayi masa addu’a shine har ya koma baki, a sakamakon haka kuma duk zuriyatasa ta zamo bakake.

Marubucin yace :- Hakika Malamai sunyi raddi akan haka, ga abinda babban malamin tarihin nan Ibn Khaldun ke cewa game da batun “Hakika waɗansu daga cikin masu nasabta abu waɗanda suke basu da ilimi dangane da kasantuwar halittu suna kawo ruɗu da cewa wai bakake ‘ya’yan Hamu ne ɗan Nuhu..

A karshe sai yake cewa wannan hikaya ce daga kissoshi masu kurakurai.

Amma dangane da addu’ar da Nuhu yayiwa ɗan nasa, Ibn Kaldun yace kissar tazo a cikin littafin Attaura, amma babu wata magana da ta nuna ya koma baki, sai dai Nuhu yayi addu’ar wa ɗan nasa ne don ya zama karamin bawan ‘yan uwansa, amma ba ya canza launin fata ba.

Bayan ɗaukewar ruwan ɗufana, sai Zangiy ya zauna a garuruwan farko na afirka, domin wajen nada albarkar noma.

Haka kuma Baban namu na bakaken fata, ya zauna a gefen kogin Nilu na kasar misra wanda kogine mai tarihi wanda ke cikin kogunan farko da Allah ya soma halitta kuma asalinsa daga kasar Uganda yake, sannan ya shigo Somaliya, eritrea da Jubuti kuma ya hauro sudan ya shigo garuruwan Nubia da suke a karkashin hukumar Asuwan ta kasar misira har a karshe ya haɗe da tekun daya wuce Iskandariya duk a kasar ta misira.

Yawan jimawar sa anan yasa kabilu daban daban suka fita daga gareshi, ciki kuwa har da Hausawa..

Dangane da dalilin watsuwar bakaken fata izuwa wannan yanki na afirka, marubucin ya tafi akan cewa Rashin zama lafiya ta dalilin mulki ne ya sanya mutane suka rinka baro danginsu.

Misali, idan uba ya mutu yabar ‘ya’yansa huɗu, a cikinsu sai suka shiga rigimar neman mulki wanda a karshe sai ɗaya ya samu nasara akan yanuwansa, to sai kaga ragowar sun tashi da iyalinsu sun shiga duniya. Don haka yace, a haka bakaken fata suka fantsama har zuwa sassan Najeriya, wasu kuma tun tale -tale sun shiga falasɗinu da sauran garuruwa domin yin kasuwanci, amma kabilar Nubiya itace bata baro misira ba, kuma har yanzu tana misira da zama a karkashin jahar Aswan.

ASALIN HAUSAWA DA DANGINSU
kabilar hausa nadaga cikin kabilun bakaken Afirka ‘ya’yan Zangiy kenan wanda ya rayu a Misira bayan ɗaukewar ruwan ɗufana.

Saboda haka asalin hausawa mazauna Misira ne waɗanda kuma suka rinka gudanar da harkokinsu acan, musamman noma, kiwo da kasuwanci.

Daga bisani sai wani yanki na tushen ƙabilar Hausa ya taso izuwa garuwan Habasha musamman yankin Dahalak, wanda yake cikin kasar Eritrea ayau. Shi wannan yanki na Dahalak har yanzu akwai hausawa masu yawa acikinsa, daga baya ne larabawa suka shiga suka zauna tare da hausawa a cikinsa.

An samu waɗansu mutane guda uku da suka fito daga waɗancan hausawa mazauna dahalak tare da iyalansu izuwa afirka ta yamma. Mutanen kuwa sune Dala, Rano, da Gaya…

Previous Post

Ban Sassauta Dokar Zaman Gida Ba, Inji El-Rufa’i.

Next Post

Wani Matashi Ya Siffanta Hancin Jaruma Rahama Da Na Mage..

Sabiu1

Sabiu1

Next Post

Wani Matashi Ya Siffanta Hancin Jaruma Rahama Da Na Mage..

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Stay Connected test

  • 23.6k Followers
  • 99 Subscribers
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Da ‘dumi’dumi: Gwamna El Rufa’i da wasu Gwamnoni na shirin ballewa ga tafiyar Bola Tinubu.

Da ‘dumi’dumi: Gwamna El Rufa’i da wasu Gwamnoni na shirin ballewa ga tafiyar Bola Tinubu.

July 19, 2022
Da ‘dumi’dumi: Babbar kotun tarayya ta bayarda Umarnin a mikawa Sanata Ahmad lawan sammaci ta ko wacce hanya domin zuwa kotu.

Da ‘dumi’dumi: Babbar kotun tarayya ta bayarda Umarnin a mikawa Sanata Ahmad lawan sammaci ta ko wacce hanya domin zuwa kotu.

July 14, 2022
Da ‘dumi’dumi Dan majalisar tarayya da na jiha tare da tsohon Minista sun fice daga Jam’iyar PDP sun koma jam’iyar NNPP ta kwankwaso Mai kayan marmari.

Da ‘dumi’dumi Dan majalisar tarayya da na jiha tare da tsohon Minista sun fice daga Jam’iyar PDP sun koma jam’iyar NNPP ta kwankwaso Mai kayan marmari.

July 15, 2022
Tonon Silili: Yadda muka shigo da ‘yan ta’addan Fulani daga Mali, Saliyo, Senegal da sauransu domin su taimaka mana a zaben 2015 – Jigon APC Kawu Baraje

Tonon Silili: Yadda muka shigo da ‘yan ta’addan Fulani daga Mali, Saliyo, Senegal da sauransu domin su taimaka mana a zaben 2015 – Jigon APC Kawu Baraje

August 3, 2022

Ina son aure yaro matashi dan shekara 25 zuwa 30~ Inji shugabar kungiyar muryar Zawarawa ta Kano

14

CBN ya rabawa Matasa mutum sama da dubu bakwai naira Biliyan biyu da digo hudu (2.04b) a karkashin tsarin NYIF.

6

Kasuwancin Cryptocurrency Haramun ne zalla ~inji Sheikh Bin Usman.

4

Duk Wanda Ya Cika Neman Bashin Ranche Karkashin Tsarin NYIF Ya Gaggauta Shiga Dashboard, Ya Sabunta Asusun Ajiyarshi Na Banki

3
Badakala: Takardu sun nuna Bashir Ahmad ya ci gaba da karbar albashi ba bisa ka’ida ba watanni bayan ya yi murabus daga mukamin mai taimaka wa Buhari kan harkokin yada labarai.

Badakala: Takardu sun nuna Bashir Ahmad ya ci gaba da karbar albashi ba bisa ka’ida ba watanni bayan ya yi murabus daga mukamin mai taimaka wa Buhari kan harkokin yada labarai.

August 16, 2022
Buhari na iya cigaba da ciyo bashi daga yanzu har abada, Amurka da Biritaniya su ma sun ci bashin kudi – Shugaban APC Adamu

Buhari na iya cigaba da ciyo bashi daga yanzu har abada, Amurka da Biritaniya su ma sun ci bashin kudi – Shugaban APC Adamu

August 16, 2022
Buhari yana kokari, mulkinsa cike yake da rashawar jami’ai, amma haka yake yaki dasu – Keyamo

Buhari yana kokari, mulkinsa cike yake da rashawar jami’ai, amma haka yake yaki dasu – Keyamo

August 16, 2022
Sanata Uba sani ya karyata batun cewa ya Kai Kudri gaban majalisar domin kirkiro Jihar zazzau.

Sanata Uba sani ya karyata batun cewa ya Kai Kudri gaban majalisar domin kirkiro Jihar zazzau.

August 15, 2022

Recent News

Badakala: Takardu sun nuna Bashir Ahmad ya ci gaba da karbar albashi ba bisa ka’ida ba watanni bayan ya yi murabus daga mukamin mai taimaka wa Buhari kan harkokin yada labarai.

Badakala: Takardu sun nuna Bashir Ahmad ya ci gaba da karbar albashi ba bisa ka’ida ba watanni bayan ya yi murabus daga mukamin mai taimaka wa Buhari kan harkokin yada labarai.

August 16, 2022
Buhari na iya cigaba da ciyo bashi daga yanzu har abada, Amurka da Biritaniya su ma sun ci bashin kudi – Shugaban APC Adamu

Buhari na iya cigaba da ciyo bashi daga yanzu har abada, Amurka da Biritaniya su ma sun ci bashin kudi – Shugaban APC Adamu

August 16, 2022
Buhari yana kokari, mulkinsa cike yake da rashawar jami’ai, amma haka yake yaki dasu – Keyamo

Buhari yana kokari, mulkinsa cike yake da rashawar jami’ai, amma haka yake yaki dasu – Keyamo

August 16, 2022
Sanata Uba sani ya karyata batun cewa ya Kai Kudri gaban majalisar domin kirkiro Jihar zazzau.

Sanata Uba sani ya karyata batun cewa ya Kai Kudri gaban majalisar domin kirkiro Jihar zazzau.

August 15, 2022
       
JaridarMikiya

We bring you the best Premium WordPress Themes that perfect for news, magazine, personal blog, etc. Check our landing page for details.

Follow Us

Browse by Category

  • Addini
  • Al'adu
  • Alqur'ani Tafarkin Tsira
  • Fina finai
  • Ilimi
  • Kasashen Ketare
  • Kasuwanci
  • Kimiya Da Fasaha
  • Kungiyoyi
  • Kunne Ya Girmi Kaka
  • Labarai
  • Lafiya
  • Mata
  • Nishadi
  • Rahotanni
  • Sana'o'i
  • Sanannu
  • Siyasa
  • Sports
  • Startup
  • Tech
  • Travel
  • Tsaro
  • Tsegumi
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • World
  • Zamani
  • Zamantakewa

Recent News

Badakala: Takardu sun nuna Bashir Ahmad ya ci gaba da karbar albashi ba bisa ka’ida ba watanni bayan ya yi murabus daga mukamin mai taimaka wa Buhari kan harkokin yada labarai.

Badakala: Takardu sun nuna Bashir Ahmad ya ci gaba da karbar albashi ba bisa ka’ida ba watanni bayan ya yi murabus daga mukamin mai taimaka wa Buhari kan harkokin yada labarai.

August 16, 2022
Buhari na iya cigaba da ciyo bashi daga yanzu har abada, Amurka da Biritaniya su ma sun ci bashin kudi – Shugaban APC Adamu

Buhari na iya cigaba da ciyo bashi daga yanzu har abada, Amurka da Biritaniya su ma sun ci bashin kudi – Shugaban APC Adamu

August 16, 2022
  • About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact

© 2022 JaridarMikiya - Design by NGWebDev.

No Result
View All Result

© 2022 JaridarMikiya - Design by NGWebDev.