• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
JaridarMikiya
Advertisement
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
    • Home – Layout 6
  • Tech

    These Are the 5 Big Tech Stories to Watch in 2017

    With 150 million daily active users, Instagram Stories is launching ads

    Trending Tags

    • Nintendo Switch
    • CES 2017
    • Playstation 4 Pro
    • Mark Zuckerberg
No Result
View All Result
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
    • Home – Layout 6
  • Tech

    These Are the 5 Big Tech Stories to Watch in 2017

    With 150 million daily active users, Instagram Stories is launching ads

    Trending Tags

    • Nintendo Switch
    • CES 2017
    • Playstation 4 Pro
    • Mark Zuckerberg
No Result
View All Result
JaridarMikiya
No Result
View All Result
Home Labarai

Abba Sadau yayan Jaruma Rahma Sadau zai Angwance.

Sabiu1 by Sabiu1
January 23, 2021
in Labarai
0
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Haruna Ibrahim Sadau, wanda ake kira Abba Sadau, shi ne babban wan su fitacciyar jaruma Rahama Sadau. A jiya Juma’a, 15 ga Janairu, 2021, Abba ya bayyana sanarwar cewa za a yi bikin auren sa a ranar 30 ga wannan watan, kuma ya na gayyatar kowa da kowa. A wani saƙon musamman da ya tura a soshiyal midiya, Abba, wanda furodusan finafinai ne a Kaduna, ya haɗa har da hotuna shida na kyakkyawar yarinyar da zai aura, waɗanda su ka ɗauka a situdiyo, wato abin da ake kira ‘pre-wedding pictures’.

Ganin wancan saƙo na Abba Sadau sai mutane su ka shiga yi wa kan su tambayoyi: Shin wace yarinya ce wannan Abba zai aura? Ya sunan ta? ‘Yar ina ce? Wane yare ce?

Kai, akwai ma masu yin tambayoyi a kan shi kan sa angon, musamman waɗanda ba su san shi sosai ba, su na faɗin shi Abban da gaske wan Rahama Sadau ne ko dai ƙanen ta ne? Shi ma ɗan fim ne? Idan wan Rahama da ƙannen ta mata ukun nan da ake gani ne, me zai ce game da auren waɗannan tsala-tsakan ‘yanmatan? Me ya sa har yanzu Rahama ba ta yi aure ba?

Mujallar Fim ta yi ƙoƙarin zantawa da Abba Sadau don samun amsoshin waɗannan tambayoyin, ciki har da yadda za a yi bikin a cikin wannan yanayi da ake ciki na cutar korona da kuma dalilin da ya sa ya riga ƙannen nan nasa yin aure. Ga yadda hirar ta kasance:

FIM: Da farko, za mu so ka faɗa mana cikakken sunan ka da tarihin rayuwar ka a taƙaice.

ABBA SADAU: Da farko dai suna na Haruna Ibrahim Sadau, wanda aka fi sani da Abba Sadau. An haife ni a Kaduna, na yi firamare da sakandare duk a Kaduna, sannan na yi jami’a a Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’Adua da ke Katsina. Na fara bautar ƙasa a Jihar Osun, daga baya na nemi dawowa Kaduna, inda a nan na ƙarasa. Kuma ni yaya ne ga jaruma Rahama Sadau.

FIM: Ga shi auren ka ya matso kusa. Yaya sunan amaryar taka?

ABBA SADAU: Sunan ta Zainab Musa Yarima, ana kiran ta da Zee Yarima.

FIM: ‘Yar wane gari ce? Kuma Bahaushiya ce ko ta na da wani yaren?

ABBA SADAU: ‘Yar nan Kaduna ce. Bahaushiya ce, amma su na da dangantaka da Maiduguri. Amma dai duk a nan Kaduna aka haife su. Kuma mun daɗe tare, aƙalla mun kai shekara takwas tare.

FIM: Me ku ka shirya yi a bikin?

ABBA SADAU: To, saboda wannan abu da ke ta faruwa na korona da sauran su, ka san Kaduna akwai doka an hana taruka da sauran su. Amma yanzu dai abin da mu ka shirya, idan aka ɗaura aure, daga wurin za mu wuce Sadauz Home a yi walima. Sai kuma mu na tunanin yin dina, in dai Gwamna ya bada damar a ci gaba da taro, tunda an ce 18 ga wata za a saki gari, za a koma makaranta, za kuma a ci gaba da ɗakunan taro, amma sai da takunkumi da sauran su. In dai ya yiwu sun buɗe ‘hall’ ɗin sun fara karɓar kuɗi, sai mu je mu biya mu yi dina, in-sha Allahu.
ABBA SADAU: To, shi wannan maganar da ma mun daɗe mu na yin shi. Kuma ka san da ma ‘ya’ya mata sai an bi a hankali, sannan duk burin uwa da uba su ga cewa sun aurar da su. A kan haka ne mu ka zauna mu ka yi mitin da ‘family’, sai aka ce, “Tunda kai ne babba, ka fara buɗawa, sai mu ga abin da Allah zai yi. Ka ga daga kan ka, in ka yi, su kuma sauran – tunda da ma da na gaba ake koyi – sai su yi.”

Wannan mitin da mu ka yi da ‘yan’uwan baban mu da sauran su kenan, su ka ce ni in fara yi. Kuma da ma ita yarinyar (Zainab), kowa a ‘family’ ya san mu tare. Nan na yarda, na ce, “Ba damuwa, ni zan fara yi.”

Da maganar da saka rana duk a cikin watan Disamba aka yi, na ce a saka wata ɗaya kawai, kada abin ya yi nisa. Ka ga daga nan sai in buɗe masu ƙofa, sai kuma mu ga abin da Allah zai yi, wataƙila ma Allah ya sa dukkan su a lokaci guda za a yi bikin nasu.

FIM: Kai ma ka na ɗan taɓa harkar fim ne?

ABBA SADAU: E to, da dai ina yi, amma daga baya-bayan nan na zo na ja jiki. Saboda wasu ‘yan dalilai da su ke faruwa sai na ga gara na daina, na cire duk wani abu na harkar fim. Duk na cire. Har a Instagram na goge duk wani abu da ya shafi harkar fim da na ɗora.

Amma a baya na yi. Duk wani fim da Rahama ta yi, ni ne furodusan shi, tun daga kan ‘Rariya’, ‘Ɗan-Iya’, ‘Mati A Zazzau’ duk mu mu ke yin komai; ita ce dai furodusa amma ba ta san abin da ake yi ba, ta na bacci, sai mu ce mata an yi kaza da kaza. Da ma da ni da Yunusa Mu’azu ne mu ke yi.

FIM: Amma ka na ganin nan gaba za ka koma?

ABBA SADAU: Gaskiya ba na tunanin komawa, na daina. Gara na ci gaba da bizines ɗi na can daban kawai, saboda na ga harkar fim ɗin ne yanzu sai a hankali, ba layi na ba ne gaskiya. Kuma ba zan iya ba. Akwai abubuwa da dama da ke faruwa wanda ba zan iya jurewa ba. A nan gaba idan aka ci gaba da haka za a iya samun matsala da ni. Ina da haƙuri sosai, amma in na fusata ba daɗi! Don haka hanyar lafiya a bi ta da sauƙi.

Kuma ban taɓa faɗa da kowa ba a industiri, kowa nawa ne. So, harkar fim ɗin ne ta koma sai kame-kame ake yi, shi ya sa na ga bari in je in nemi wata sana’ar kawai. Na ga ina da digiri, kawai bari in je in ci gaba da buge-buge na tunda na san hanyoyin kasuwanci iri-iri.

FIM: Abba, mun gode. Daga FilmMagazine

Previous Post

A ƙoƙarinsa na tabbatar da Dimokuradiyya da ‘yancin talaka, shugaba Buhari ya bawa gwamnoni umarnin rushe shuwagabannin ƙananan hukumomi na riƙo, tare da maye gurbinsu da zaɓaɓɓu.

Next Post

Kungiyar Arewa Media Writers ta yi Allah wadai da harin ta’addacin da Matasan Yarbawa suka kaiwa Sarkin Fulanin Jihar Oyo, a gaban jami’an tsaron jihar.

Sabiu1

Sabiu1

Next Post

Kungiyar Arewa Media Writers ta yi Allah wadai da harin ta'addacin da Matasan Yarbawa suka kaiwa Sarkin Fulanin Jihar Oyo, a gaban jami'an tsaron jihar.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Stay Connected test

  • 23.6k Followers
  • 99 Subscribers
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Burin murtala garo na zama Gwamnan Kano ya ruguje, ya hau jirgi ya bi Ganduje kasar Dubai domin neman goyon bayansa kafi ya ajiye mukamin kwamishina.

Burin murtala garo na zama Gwamnan Kano ya ruguje, ya hau jirgi ya bi Ganduje kasar Dubai domin neman goyon bayansa kafi ya ajiye mukamin kwamishina.

April 2, 2022
An garzaya da Buba Marwa Asibitin kasar London kwanaki ka’dan Bayan DIG mai Binciken DCP Abba kyari ya mutu.

An garzaya da Buba Marwa Asibitin kasar London kwanaki ka’dan Bayan DIG mai Binciken DCP Abba kyari ya mutu.

March 15, 2022
TSARO: Maganar gaskiya Buhari bashi da imani bashi da tausayi, Allah ya Isa Tsakanin mu da azzalumin Shugaba ~Cewar Ali madaki.

TSARO: Maganar gaskiya Buhari bashi da imani bashi da tausayi, Allah ya Isa Tsakanin mu da azzalumin Shugaba ~Cewar Ali madaki.

March 30, 2022
DA ‘DUMI ‘DUMI: EFCC ta gano yadda Gwamna Tambuwal yayi kwana da Naira Bilyan 189.1bn zuwa ga wasu asusun ajiyar bankuna.

DA ‘DUMI ‘DUMI: EFCC ta gano yadda Gwamna Tambuwal yayi kwana da Naira Bilyan 189.1bn zuwa ga wasu asusun ajiyar bankuna.

April 2, 2022

Ina son aure yaro matashi dan shekara 25 zuwa 30~ Inji shugabar kungiyar muryar Zawarawa ta Kano

14

CBN ya rabawa Matasa mutum sama da dubu bakwai naira Biliyan biyu da digo hudu (2.04b) a karkashin tsarin NYIF.

6

Kasuwancin Cryptocurrency Haramun ne zalla ~inji Sheikh Bin Usman.

4

Duk Wanda Ya Cika Neman Bashin Ranche Karkashin Tsarin NYIF Ya Gaggauta Shiga Dashboard, Ya Sabunta Asusun Ajiyarshi Na Banki

3
Ƙalubale Gareku ‘Yan Najeriya: Hukumar EFCC ta koka da karancin masu fallasa, duk da dimbin tukuicin da take bayarwa.

Ƙalubale Gareku ‘Yan Najeriya: Hukumar EFCC ta koka da karancin masu fallasa, duk da dimbin tukuicin da take bayarwa.

June 30, 2022
Kokarin Buhari Na Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Talauci: Gwamnatin Tarayya ta shirya kwashe almajirai akalla 1,000 a kan titin Abuja.

Kokarin Buhari Na Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Talauci: Gwamnatin Tarayya ta shirya kwashe almajirai akalla 1,000 a kan titin Abuja.

June 30, 2022
Sallah: Ministan Abuja yavyi gargadi ga masu sayar da raguna a Abuja.

Sallah: Ministan Abuja yavyi gargadi ga masu sayar da raguna a Abuja.

June 30, 2022
Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rarraba Kayayyakin Koyo Kyauta Ga Dalibai.

Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rarraba Kayayyakin Koyo Kyauta Ga Dalibai.

June 30, 2022

Recent News

Ƙalubale Gareku ‘Yan Najeriya: Hukumar EFCC ta koka da karancin masu fallasa, duk da dimbin tukuicin da take bayarwa.

Ƙalubale Gareku ‘Yan Najeriya: Hukumar EFCC ta koka da karancin masu fallasa, duk da dimbin tukuicin da take bayarwa.

June 30, 2022
Kokarin Buhari Na Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Talauci: Gwamnatin Tarayya ta shirya kwashe almajirai akalla 1,000 a kan titin Abuja.

Kokarin Buhari Na Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Talauci: Gwamnatin Tarayya ta shirya kwashe almajirai akalla 1,000 a kan titin Abuja.

June 30, 2022
Sallah: Ministan Abuja yavyi gargadi ga masu sayar da raguna a Abuja.

Sallah: Ministan Abuja yavyi gargadi ga masu sayar da raguna a Abuja.

June 30, 2022
Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rarraba Kayayyakin Koyo Kyauta Ga Dalibai.

Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rarraba Kayayyakin Koyo Kyauta Ga Dalibai.

June 30, 2022
       
JaridarMikiya

We bring you the best Premium WordPress Themes that perfect for news, magazine, personal blog, etc. Check our landing page for details.

Follow Us

Browse by Category

  • Addini
  • Al'adu
  • Alqur'ani Tafarkin Tsira
  • Fina finai
  • Ilimi
  • Kasashen Ketare
  • Kasuwanci
  • Kimiya Da Fasaha
  • Kungiyoyi
  • Kunne Ya Girmi Kaka
  • Labarai
  • Lafiya
  • Mata
  • Nishadi
  • Rahotanni
  • Sana'o'i
  • Sanannu
  • Siyasa
  • Sports
  • Startup
  • Tech
  • Travel
  • Tsaro
  • Tsegumi
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • World
  • Zamani
  • Zamantakewa

Recent News

Ƙalubale Gareku ‘Yan Najeriya: Hukumar EFCC ta koka da karancin masu fallasa, duk da dimbin tukuicin da take bayarwa.

Ƙalubale Gareku ‘Yan Najeriya: Hukumar EFCC ta koka da karancin masu fallasa, duk da dimbin tukuicin da take bayarwa.

June 30, 2022
Kokarin Buhari Na Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Talauci: Gwamnatin Tarayya ta shirya kwashe almajirai akalla 1,000 a kan titin Abuja.

Kokarin Buhari Na Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Talauci: Gwamnatin Tarayya ta shirya kwashe almajirai akalla 1,000 a kan titin Abuja.

June 30, 2022
  • About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact

© 2022 JaridarMikiya - Design by NGWebDev.

No Result
View All Result

© 2022 JaridarMikiya - Design by NGWebDev.