Labarai

Hukumar, NDLEA, ta fara fitar da sunayen mutum 5,000, da ta dauka aiki,

Spread the love

Hukumar, yaki da hana ta’ammali da miyagun kwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ta ce ta fitar da sunayen wadanda suka samu nasarar a ci gaba da daukar ma’aikata da ta keyi,

Kakakin hukumar Jonah Achema, ne ya bayyana cikin wata sanarwa da ya aike wa kamfanin dillancin labarai na kasar nan a ranar Juma’a,

Mista Achema, ya shawarci wadanda suka nemi aikin da su ziyarci shafin hukumar na Intanet www, NDLEA gov-org domin ganin karin sunayen da aka wallafa bayan wadanda aka tuntuba ta sakon karta kwana da kuma Email,

A cewarsa mutane da dama sun nemi wannna aiki a kuma matakai daban-daban wasu ma har an kirasu domin su je a musu jarrabawa,

Wadanda aka tuntuba su, 5,000 za su je ma’aikatar CCNN da ke jihar Plateau domin tantance su tare da takardunsu, kuma za a fara ne tsakanin 10: ga watan janairun da muke ciki zuwa 23: ga watan za a rika fara, aiki a Kullum daga karfe 09:00: na safe

za a raba masu neman aikin zuwa kashi hudu domin aikin tantancewa, domin tabbatar da an bi dokar da kuma ka’idojin wannna annoba ta Covid-19: in ji mista Achema, Daga Abbakar Aleeyu Anache,

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button