Labarai
Zamu koyawa al’umma kiwon Jajayen Awakai idan na zama Gwamnan jihar Kaduna ~Cewar Isah Ashiru kudan.

Dan takarar Gwamnan jihar Kaduna karkashin jam’iyar PDP Isah Ashiru kudan a wani Bidiyo dake yawo a Kafafen sada zumintar zamani an hangoshi Yana cewa akwai bangaren da bai tabo ba a harkokin noma wato yanayin da za’a koyawa mutane yanayin kiwon jajayen Awakai.
Labarin daya jawo CeCe kuce ga Dan takarar Gwamnan jihar na Kaduna musamman abokan adawa na jam’iyar APC na ganin rashin wayewar zamani na damun Dan takarar musamman idan aka ha’da shi da Dan takarar Gwamnan jam’iyar APC Sanata Uba sani Wanda tun ya Samar da hanyoyin kiwon ga matasa a matakin duniya daidai da zamani.
Isah Ashiru kudan jama’a da dama na Masa kallon karancin ilimi da Zama Gwamna Kamar na Jihar Kaduna.