Labarai

Labaran Yammacin Lahadi 10/05/2020CE – 17/0/1441AH.

Spread the love

Daga Haidar H Hasheem Kano

Hukuma NCDC ta ce an samu karin cibiyoyin gwajin cutar Covid-19 guda uku a Najeriya.

Gwamnatin jihar Legas ta ce karin mutum 21 sun warke daga cutar Coronavirus.

Dokar Kulle: Kamfanonin sufuri masu zaman kansu sun ce sun yi asarar Naira Trilyan 3 a tsawon makonni 5 na dokar a Najeriya.

Al’ummar Fulani a jihar Delta sun bukaci a biya su diyyar kona masu gidaje da aka yi.

Gwamna Wike na jihar Rivers ya jagoranci rushe wasu Otal 2 da suka karya dokar kulle a Fatakwal.

An samu karin mutum karin 7 da suka warke daga cutar Coronavirus a Abuja.

Wasu mutane 2 masu dauke da cutar Coronavirus sun tsere a Kaduna.

Sheikh Bala ya karyata rahotannin mutuwarsa da ake yadawa, ya ce yana nan lafiyarsa lau.

Covid-19: Wadanda suka kamu da cutar sun zarta 200,000 a Rasha.

Ministan lafiyar Jamhuriyar Kamaru, Malachie Manaouda ya ce kasar na da mutum 2579 masu dauke da cutar Covid-19.

An kaiwa Masallaci hari da duwatsu a garin Cologne da ke Jamus.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button