Rahotanni

MAI HANKALI SHIKE GANE FURFURAR FARAR TUNKIYA

Idan ka ɗauki gwamnatin Shugaba Buhari rankacakaf! ka ɗorata a bisa mizanin gaskiya da adalci babu wani abu ɗaya tilo wanda mutum zai bugi ƙirji ya nuna a matsayin abin da talaka ɗan talaka mai siyar da yalo da goba yake amfana kai-tsaye face shirin N-POWER.

-A ƙarƙashin shirin matasa da yawa sun bar zaman kashe wando sannan sun samu aikin dogaro dakai

-A ƙarƙashin shirin ilmi ya farfaɗo sakamakon yadda makarantu suka samu wadatattun malamai masu jini a jika.

-A ƙarƙashin shirin matasa da yawa suke kulawa da iyalansu, iyayensu tare da taimakawa ƴan uwansu.

-Ƴan N-Power da yawa sunyi rawar gani ta fuskar kawo cigaba da magance matsalolin garuruwansu

-Ƴan N-Power da yawa basu da wani abu da suke ciyar da iyalansu sai ta alawus ɗin da suke samu duk wata.

-Ƴan N-Power da yawa sun samu horo da gogewa ta fuskar koyarwa , shi yasa ɗalibai suke samun ilmi ingantacce a makarartunmu

-Korar ƴan N-power babbar barazana ce ta fuskar zaman lafiya da tattalin arziƙin ƙasa

-Korar ƴan N-Power zai iya kawo cikas ga fannin ilmi a ƙasa

Duba da irin waɗannan abubuwan dana zayyana a sama, Duk da bana cikin shirin N-Power ina ganin ba karamin kuskure bane a kori bayin Allah nan a rana tsaka. Gwamnatin Najeriya ta yiwa matasan nan adalci a matsayinsu na ƴan ƙasa ta barsu su cigaba da aikinsu ko kuma gwamnatocin jahohi su duba Allah su basu aikin yi na din-din-din.

Tabbas ƙara ɗaukar sababbin ƴan N-power abu ne daya dace amma korar waɗanda suke cikin shirin ba ƙaramin kuskure bane da cefa al’umma cikin ƙuncin rayuwa musamman ma matasa manyan gobe.

Daga Mutawakkil Gambo Doko

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button