Masu kalaman batanci A yanar gizo zasu biya Gwamnatinmu milyan biyar N5m Lai Mohammed
Gwamnatin Tarayya ta ce ta kara kudin Tarar kalaman batanci da nuna kyama daga N500,000 zuwa miliyan N5 a cikin Dokar Watsa labarai ta Kasa don hana mutanen da suka yi niyyar karya tattalin arzikin kasar. Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya ba da wannan bayanin ranar Juma’a lokacin da ya gabatar da wani shiri a gidat TV na TVC Shirin mai suna, This Morning”. Lai ya kasance a cikin shekarar 2019 ya ba da sanarwar amincewar shugaban kasa Muhammadu Buhari game da karin kudin da aka sanya a baya wanda aka sanya a cikin kundin yada labarai na gyara. “Abin da ya motsa yin kwaskwarimar shi ne lokacin da muka ga ana iya biya kudin N500,000 cikin sauki shine muka kara shi Ya yi bayanin cewa wasu mutane masu matsananciyar Adawa wadanda suka san cewa kayan aikinsu na watsa shirye-shirye sun kunshi kalaman nuna kiyayya, za su nace cewa ya kamata tashar watsa shirye-shiryen ta watsa ta yayin da suke biyan kudin. Ministan ya lura cewa wadanda ke kai hari kan gwamnati kan kara kudin, dole ne su tuna cewa kalaman kiyayya sun lalata kasashe da dama. Ya tuna cewa Rwandan sun rasa rayukan 800,000 saboda kalaman nuna kyama yayin da Bosniya da Kambodiya suma suka rasa dubban rayukan da ke cikin hadarin.
Mohammed ya ce Najeriya ba ita ce kasa kadai da za ta kakaba takunkumi kan kalaman nuna kyama ba, ya kara da cewa wasu kasashe na da tanade-tanade. “A yau kasar Chadi ta rage saurin ayyukan ta na intanet domin rage ci gaban kalaman nuna kiyayya. Iceland ta tanadi tanade-tanaden doka game da kalaman kiyayya kuma hukuncin yana da shekaru biyar a gidan yari. “Takunkumi a kasar Norway ya kai shekaru biyu a kurkuku yayin da Afirka ta Kudu ta ware kalaman nuna kiyayya daga kariyar da ‘yan kasarsu za su samu daga kundin tsarin mulki,” in ji shi. Ministan ya ce kalaman kiyayya ba wani sabon abu bane amma kafofin sada zumunta da kuma karfin ikonta na yada labarai ne ya sanya ta zama matsala. Don haka, ya sake nanata kudirin gwamnati na daidaita kafofin watsa labarun ba tare da hana ‘yancin fadin albarkacin baki ba.