Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta kama wani babban jami’in hukumar Hisbah na Kano tare da matar aure a Otal.
Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta cafke wani babban jami’i a hukumar Hisbah ta jihar bayan an kama shi tare da matar aure a wani otal.
A cewar Freedom Radio Kano, an kame jami’in a yankin Sabon Gari da ke cikin birnin Kano. Ba a ambaci sunan jami’in ba.
An ce jami’in da aka kama shi ne mai kula da kama mabarata da karuwai a yankin garin na Kano. An kama shi ne bayan mijin matar da ake zargin ya yi fada da ita ya shigar da kara.
A cewar gidan rediyon, Kwamandan Hisbah na Kano, Muhammed Haruna, yayin da yake bayyana lamarin a matsayin abin takaici, ya ce an kafa kwamiti na mutum biyu da zai binciki lamarin.
Jami’an Hisbah a kai a kai suna kame mutanen da ba su da aure wadanda aka kama a cikin otal-otal, mai yiwuwa don yin lalata, a zaman wani bangare na aiwatar da Shari’a.
An kafa ta ne don aiwatar da Shari’a, kwanan nan Hisbah ta hana aski mai salo, suwaga da wando, kade-kade a yayin taron jama’a ta hanyar jockey disk sannan ta kwace babura masu kafa uku daga masu tuka su saboda adonsu da hotunan da ake ganin na batsa ne kuma ya sabawa dokokin addinin Islama a wasu jihar Kano.