Tsaro

Sojoji da boko haram sunyi luguden wuta

Spread the love

Majiyar ta tabbatar mana da cewa an kashe mayakan Boko Haram bakwai a yayin harin wanda ya kwashe awanni biyu. Haka kuma an kashe wani yaro farar hula mai shekaru biyar, wanda harsashi ya tashi. SaharaReporters sun tattaro bayanai  cewa gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, yana garin Damasak a ranar Laraba don rarraba kayan agaji ga mutanen da suka rasa muhallinsu a garin. Rikicin Boko Haram ya haddasa mutuwar mutane sama da 35,000 tun daga shekarar 2009. Kungiyar ta’addanci tana son khalifancin Musulunci a Arewacin Najeriya. Duk da haka, an an dakile  ayyukan ta a jihohin na Arewa maso Gabas guda uku, wato Adamawa, Borno da kuma  Yobe saboda kokarin hukumomin tsaro.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button