Tsaro

Ta’addanci: ‘Yan Boko Haram Sun kashe Babban Malami a Borno.

Spread the love

A jiya laraba ne mayakan Boko Haram suka kashe mutane 5 cikinsu hadda limamin garin.

Lamarin ya faru ne a garin Banki dake karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

Mayakan sun shiga garin bankin ne da misalin karfe 7 na daren jiya, Inda suka kashe mutane 5 da babban Malamin Garin.

Mayakan Boko Haram din dai suna cigaba da cin karensu ba babbaka a yankin Arewa Maso gabashin kasar.

Sai dai Kungiyar tayi Ikirarin Kafa Sansani a Yankin Arewa ta Tsakiya da Arewa maso yammacin Kasar Nan.

Ahmed T. Adam Bagas

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button