Zamu hukunta Duk Wanda muka Kama ya bude islamiyya A Kano, Gwamnatin jihar kano
A cewar Kwamishinan ilimi Na jahar Kano
Kwamishinan ilimi Na jahar Kano sunusi maji Dadi ‘kiru yace zasu hukunta Duk wani malami da Suka Kama ya karya doka wajen bude makarantun islamiyya A jahar Kano
Yace ba daedae bane A lokacin da cutar cobid-19 take ‘karuwa A nijeriya Ace za’a bude makarantun islamiyoyi
Ya ‘kara da cewa bude makarantun islamiyoyi A wanan lokacin zai jefa rayuwar dalibai cikin hatsari inda ya gargadi malaman makarantun islamiyoyi da kada Wanda ya kuskura ya bude makaranta har sai humumar ilimi ta jahar Kano ta bada umarnin haka Duk Wanda muka Kama ya karya Mana doka zamu dauki tsatstsauran hukunci A kansa A cewar majidadi ‘kiru
Kwamishinan Yana wanan jawabine Kai tsaye A tashar rediyo ta vision dake Kano yayi da yake amsa tambayoyi Akan batun komawa makaranta